Tuesday, December 25, 2007

Lalacewar ’Yan Nijeriya Ta Kai Inda Ta Kai Ne?



Kwanan baya na hau bas daga wata unguwa a cikin garin Abuja zuwa inda ofishin da nake aiki yake. Kafin in hau sai da kwandastan (conductor) bas d'in ya shaida mini kud'in da zan biya, na kuma amince.
Lokacin da muka iso Kasuwar Wuse, fiye da rabin fasinjojin bas d'in suka sauka, kwandasta ya d'ebi wasu sabbi. Kasancewar nisan Kasuwar Wuse da inda zan sauka kusan rabin tafiyar daga inda na hau ne, babu mamaki idan kudi'n motar sabbin fasinjojin ya kasance rabin nawa.
Ba a jima da fara tafiya ba, sai kwandsta ya nemi mu biya kud'in mota. Na d'auko kud'i na bashi. Abin da na bayar daidai abin da ya shaida mini ne tun da farko. Amma sai kwandastan ya yi zaton daga Wuse na hau, don haka ya 'kirgo canji ya bani. Ni kuwa sai na mayar masa da canjinsa na ce “ai ba daga Wuse na hawo ba”.
Ganin haka sai fasinjan da ke kusa da ni ya yi mamaki, ya ce “lallai kai d'an 'kasa ne na gari”. Amma ni ban ga wani abin mamaki ba a wannan al’amari.
Bayan an kwana biyu sai na sake hawa mota—wannan karon tasi—daga kusa da gidan da nake zaune zuwa wajen aiki na. Lokacin da na iso tashar da zan hau mota sai na samu motar da ke lodi ba kowa, don haka na samu damar hawa gaba. Wata 'kila saboda yawan 'karin kud'in mai da aka yi ta yi direboda suka yi ta 'korafin cewa ba su samu su mayar da kud'in jigila balle su samu riba, ba ba'kon abu bane a Nijeriya ka ga an d'auki fasinja biyu a gaba, hud'u a baya. A Abuja, saboda sa-idon da jami’an Hukumar Kare Had'urra ta 'Kasa (Federal Road Safety Commission [FRSC]) ke yi musamman wajen ganin an yi amfani da d'amarar kujera (seat belt), a kan d'auki mutum d'aya ne a gaba, hud'u a baya.
Ina zaune a mota har ta kusan cika, saura mutum d'aya. Can sai ga mutum d'aya ya zo, amma fa yana da 'kiba sosai, don haka sauran wajen da ya saura a bayan mota ya yi masa kad'an. Nan aka fara sa'ke-sa'ken yadda za a yi. Wasu su ka bayar da shawarar cewa ya jira motar da za ta yi lodi ta gaba, shi kuma ya ce tun da ya yi sa’a ya samu mai tafiya nan take baya sha’awar zama jiran sai wata motar ta cika.
Nan fa direban motar ya zo ya same ni a kan in yi ha'kuri in koma baya, in ya so wannan mutumin mai 'kiba ya hau gaba. Ganin akwai hikima a yin hakan—tun da ni ba wata 'kiba ba ce da ni—sai na sauka na koma baya ba tare da na yi musu ba. Hakan ya janyo mini yabo daga fasinjojin motar, wad'anda suka ce lallai ni d'an 'kasa ne na gari.
Wad'annan abubuwa biyu da suka faru suka sanya na fara tunanin cewa "shin lalacewar 'yan Nijeriya ta yi matu'kar tsanani ne da har in mutum ya aikata gaskiya ko ya yi taimako za a ri'ka yabonsa haka?" Ni a ganina dukkan addinan da 'yan Nijeriya suke yi sun yi horo da aikata gaskiya, da kuma taimakon juna. A sanina ga Musulmi Al-'Kur’ani ya yi horo ba kawai a aikata gaskiya ba, a ma kasance da masu gaskiya. Sannan kuma tarihi ya nuna cewa taimakon da Manzon Allah (Tsira da Amincin Allah su tabbata a gareshi) ya yi wa wata tsohuwa shi ya sanya ta ta musulunta duk da ta kasance mai 'kin sa (shi Manzon).
Haka ma abin yake a addinin Kirista, inda Littafin Baibul ya ce ri'kon gaskiya na sanya al’umma ta d'aukaka. Sannan kuma ya ce, a wani wuri na daban, ka kasance mai tallafawa d'an-uwanka. Kai ko mutum ba ya yin addini, wad'anda babu ruwansu da addini suna nuni da cewa su masu 'kaunar d'an-Adam ne don haka a ko yaushe a shirye suke su taimaki mutane. Amma ga alama 'yan Nijeriya sun manta da duk wannan.
Baya ga addini, babu mamaki kasancewa ta d'an arewa ya taimaka wajen ganin cewa abin da na yi ba wani abin a-zo-a-gani ba ne. A ma'kalar da ya ke rubutawa duk mako a jaridar Weekly Trust, Segun Odegbami ya ta'ba cewa zaman da ya yi da 'yan arewa ya gane cewa su mutane ne masu tsantseni, da wadatar zuci, da kuma rashin had'ama. Idan dai aka je aka zo, za a dawo kan maganar addini domin wad'annan halaye na 'yan arewa ko shakka babu sun samo tushe ne daga tasirin da addini (musamman Musulunci) ya yi a rayuwarsu. Addini ya sa mutumin arewa ba shi da wuyar rungumar 'kaddara. Sau da yawa za ka ga wasu sun tafka asara wadda a sanadiyyar ta sun suma ko ma sun she'ka barzahu, amma d'an arewa idan ya tafka irinta sai ka ji ya ce “Haka Allah Ya so”, ya ci gaba da harkokinsa. Ko da zai yi ba'kin ciki, zuwa wani lokaci sai ya manta.
Ga wanda ya san al'adar Malam Bahashe, misali, ya san cewa idan aka yi mutuwa ya kan je ya yi gaisuwa. Gaisuwar kuma ba ta wuce: “Ya (aka ji da) ha’kuri?” ba. Martanin da wanda aka yiwa rasuwar yake mayarwa shine: “Ha'kuri ya zama dole” ko kuma “Ha'kuri sai Ma’aiki (Manzon Allah)”. Abin nufi shine: “Manzo ya karantar da mu mu yi ha'kuri da duk abin da Allah Ya d'ora mana”.
Kwanan nan kafofin yad'a labarai suka ruwaito labarin wani mutum da ya tsinci kud'in da suka kai kimanin miliyan tamanin na nairori (N80,000,000), da kuma wata 'yar 'Kato-Da-Gora (Nigeria Security and Civil Defence Corps) wadda ta tsinci dubban nairori a mota, amma suka nemi masu kud'ad'en don su mayar masu da abinsu. Nan take na tuna kwana bakwai kacal kafin faruwar haka na shaida zage-zage da aka yi tsakanin direban tasi da fasinjansa a kan naira goma (N10.00) kacal. A 'ka’idar 'yan tasi akwai kud'in da za a biya zuwa ko wanne wuri. Kuma ana amfani da sunan wurin tsayawar bas (bus stop) na bakin titi a wurin. Ke nan ana wuce wurin tsayawa, kud'i ya 'karu. A haka ne shi wannan fasinja za shi wani wuri, in an wuce inda ya fad'a, amma nisan bai fi taku d'ari biyu ba daga wurin tsayawa na baya. Lokacin da aka iso wurin tsayawar da fasinja ya ambata sai direba ya ja birki; shi kuma fasinja ya ce ba a zo inda zai sauka ba. Direba ya ce muddin ya 'ketare wannan wuri sai fasinja ya 'kara kud'i har naira goma. Fasinja kuma ya ce shi sam ba zai sauka ba sai an 'karasa da shi, kuma ba zai 'kara ko kwabo ba. Sauran fasinjojin da ke motar suka fara mita a kan ana 'bata masu lokaci, sai direba ya ce in har ya motsa da fasinjan nan ba zai tsaya a inda fasinjan zai sauka ba. Ya kuwa fizgi mota zai yi gaba. Isowa inda zai sauka ke da wuya, sai fasinja—dama a gaba ya ke kusa da direba—ya yi wuf ya ri'ke sitiyari, mota ta fara tangal-tangal. Nan fa aka tsaya ana ta cacar baki, har aka kusa a ba hammata iska—duk a kan naira goma. Wannan ke nan: son banza, da rashin wadatar zuci, da rashin ha'kuri, da ma son cuta abubuwa ne da suka zama ruwan dare a tsakanin 'yan Nijeriya.
Ga kuma talauci da ya yi wa al'ummar 'kasar 'kofar rago. Mutum ba zai fahimci irin 'kuncin rayuwa da 'yan Nijeriya ke fama da shi ba sai ya je wasu unguwanni a gefen birnin Abuja. Duk da rusau d'in da el-Rufa’i ya yi kusan shekaru hud'u ya na yi a Abuja akwai wuraren da mutane ke kwana a rumfunan kara wad'anda 'kwa'k'kwarar iska za ta iya d'aukewa. Kai wasu ma a 'kar'kashin gadar fly-over su ke kwana. Ga wanda bai san fly-over ba, ita ce hanyar motar da ta wuce ta saman wata hanyar don ba a son samun cinkoson motoci. Idan ba na manta ba na ta'ba jin wani mtumin yankin Naija Delta yana 'korafin cewa yawan gadar fly-over da ke Abuja ya fi yawan gadojin da suka 'ketare rafuka da 'koramu a yankin wanda daga nan ne Nijerya ta ke samun kaso mafi tsoka na kud'in shigar ta.
Amma fa kar a manta cewa el-Rufa’i ya ce ba don talakawa aka yi Abuja ba.

Friday, December 14, 2007

JASAWA SUN BARA


Lokacin da Jasawa suka yanke shawara su 'ki fitowa aiki ko kasuwa don nun rashin jin dad'insu da abin da suka kira halin ko-in-kula da gwamnatin Jihar Filato take nunawa ga al'amuran da suka shafe su, abin ya baiwa kowa mamaki.
Hasali ma tasirin wannan ho'b'basa ya girgiza Jihar gaba d'aya, kama daga gwamnati har zuwa talakawa. Ba zato ba tsammani kawai aka wayi gari babu kowa a kasuwa babu wanda ya bud'e shago, babu motoci a tituna. A karon farko al'ummar Jasaw suka yanke shawarar d'aukar mataki kuma kowa ya bayar da had'in kai sa'banin yadda abin yake a can baya.
Daga cikin abubuwan da Jasawa suke adawa da su da suka sanya su d'aukar wannan mataki akwai yun'kurin da Gwmanan Jihar, Da David Jinah Jang ya ke yi an tshin sakatariyar 'Karamar Hukumar Jos ta Arewa daga inda take a yanzu ya mayar da ita ofishin Hukumar Tsabtace Garin Jos (Jos Metropolitan Development Board [JMDB]).
Al'ummar Jasaswa na ganin cewa d'auke sakariyar daga inda take a yanzu a mayar da ita wani waje mataki ne da gwmnatin ke 'ko'karin d'auka don nesanta su da harkar mulki a 'karamar hukumar kwata-kwata. Sanin kowa ne cewa wurin da sakatariyar take a yanzu wuri ne da Jasawa ke tin'kaho da shi a matsayin nasu-ko ba komai su kan ri'ka jin duk wani 'kwa'k'kwaran motsi da aka yi. Amma idan sakatariyar ta bar wajen shi ke nan sai a ri'ka yi babu su.
Dalili na biyu da ya sa Jasawa ba su amince da d'auke sakatariyar ba shi ne shirin da aka ce Gwmna Jang yana yi na gina wata 'kasaitacciyar majami'a a wurin da sakatariyar take. Hujjar Gwamnan ta yin hakan, kamar yadda wasu majiyoyi suka ruwaito, itace cewa a garuruwan sarakunan arewa za ka samu a kusa da fadar sarki akwai masallacin Juma'a. Don haka ya ke ganin ya kamata a ce a kusa da fadar Gbong Gwom (Sarkin Birom) wadda take kusa da sakatariyar akwai katafariyar majami'a.
Sai dai al'ummar gari suna gani rashin dacewar wannan hujja domin a cewarsu Gbong Gwom din nan, tun ma kafin rikicin da yayi kaca-kaca da garin Jos a shekarar 2001, ba ya kwana a wannan fadar. Saboda haka, a ganisu, akamta ya yi a tafi ko ma ina ya ke kwana a gina masa majami'a. Sannan kuma tarihi ya nuna cewa kusa da inda fadar Gbong Gwom d'in take, nan ne asalin fadar Sarkin Jos Isiyaku, wanda yake Bahaushe ne, kafin Turawan mulikin mallaka su kar'be sarautar su baiwa Rwang Pam. Bugu da 'kari kuma Jasawa suna ganin cewa tun da a yanzu 'yan 'kabilar Birom d'in da ke 'karamar hukumar Jos ta Arewa ba su da yawa, kamata yayi a d'auke fadar Gbong Gwom d'in gaba d'ayanta a mayar da ita inda mabiyansa ke da rinjaye.
Ko da yake wannan yajin fita da Jsawa suka yi ya yi matu'kar nasara da tasiri, an samu wasu balgurbi da suka nemi a yi wa al'amarin 'kafar ungulu. Daga cikinsu akawai wani wasu 'yan siyasa da suka shiga gari suna surutai suna sukar shugabannin al'umma. Wad'annan mutane, idan ab su yi a hankali ba, na fuskantar barazanar rasa samun kwanciyar hankali a tsakanin al'umma domin kuwa kowa na yi musu tofin Allah-tsine. A cikinsu akwai wanda aka ba shi wani mu'kami da ke da muhimmanci ga rayuwar ibadar Muslmi. Kuma wata majiya ta ruwaito cewa an bshi wannan mu'kami saboda an san cewa shi lalatacce ne, wanda zai iya had'a baki don cutar da al'ummarsa matu'kar zai samu d'an abin miya.
Hausawa dai na cewa "In rana ta fito tafin hannu bai iya kare ta" sannan kuma "Kowa ya daka rawar wani to tasa za ta 'baci". In kunne ya ji....