Monday, December 01, 2008

Hannuwan Jang Sun Yi Jina-jina

Zai yi wuya a ce, ya zuwa yanzu, akwai wanda bai samu labarin hatsaniyar da ta hargitsa garin Jos ba, inda aka kashe d'aruruwan mutane, mafi yawancinsu da harsashin 'yan sanda. Wasu mutanen da aka kashe ma ba mazauna garin Jos ba ne, wucewa kawai su ka je yi. Haka kuma zai yi wuya a ce akwai wanda bai ji irin zarge-zargen da mahukunta a Jihar Filato su ke ta yi ba—cewa wannan yamutsi shirya shi aka yi don hana garin, da ma Jihar, zaman lafiya.
Babu shakka, za mu iya yarda ba tare da wata-wata ba, cewa wannan aika-aika an dad'e da shirya aikata ta. Sai dai abin tambaya shi ne, su wanene su ka shirya ta? Don amsa wannan tambaya muna bu'katar yin wasu 'karin tambayoyi ko ma iya fahimtar al’amarin a muhallin da ya dace.
Da farko, su wanene su ka fito fili su ka ce tun da a wasu jihohi jam’iyyar da ke mulki ce ta lashe za'ben dukkan 'kananan hukumomi, wajibi ne a Jihar Filato ma hakan ta kasance, ko da kuwa sama da 'kasa za su had'u? Sannan su wanene su ka fito fili su ka ce ba za su sake yarda wani mutum daga wata al’umma ya sake mulki a 'Karamar Hukumar Jos ta Arewa ba, ko da kuwa wannan al’ummar ita ke da rinjaye? Bayan wannan su wanene suka d'auke wurin tattara sakamakon za'be daga Sakatariyar 'Karamar Hukumar Jos ta Arewa, inda a nan ne aka saba tattarawa, su ka mayar can bayan gari, ihun-ka-banza (don su samu sakewa su yi magud'i yadda su ke so)? Su wanene su ka lashi takobin 'kwace garin Jos 'karfi da yaji don su samu damar cin zarafin wata al’umma wadda da jininta da guminta aka kafa garin har ya bun'kasa ya kai inda ya kai yanzu?
Kafin mai karatu ya amsa wad'annan tambayoyi, ga wani bayani kad'an game da mutumin da a halin yanzu ya ke ri'ke da ragamar gwamnatin Jihar Filato (a 'kar'kashin kulawarsa komai ya faru), wanda a ko yaushe ya ke tutiyar cewa yana son Jihar ta zauna lafiya. Wad'anda suka san Jonah David Jang sun ce shi Kirista ne irin wad'anda su ke kiran kansu born again (in ka so ka ce ‘yan gani-kashe-nin Kiristanci). Wannan tsatstsauran ra’ayin Kiristancin ne ya sa bayan ya hau mulki ya haramtawa mata masu nuna tsiraicinsu shiga gidan gwamnati da ma sakatariyar gwamnatin Jihar. Ko da ya ke an ce kasancewarsa born again ta sa ba ya shan barasa, amma idan ka dubi idanuwansa da kyau za ka ga alamar a da ya d'an ta'ba.
Wani abu da ya kamata mu fahimta da Jang shi ne cewa shi fa ba kamar sauran 'yan siyasa ba ne. A baki duk wani d'an siyasa ya kan ce yana neman mulki ne don yi wa talaka aiki; a aikace kuma yana yi ne don cika aljihunsa kawai. To amma shi Jang babban ginshi'kin siyasarsa shi ne 'kiyayya ga Musulmi, musamman Hausawa, da addininsu na Musulunci. Cin zarafinsu kuma shi ne manufarsa ta neman mulki. 'Kasa kad'an da wannan manufa kuma akwai burin ganin ya 'kwato duk wasu madafin iko a Jihar Filato ya dan'ka a hannun 'yan 'kabilarsa ta Birom, wad'anda kafin shi ba su ta'ba samu an za'bi wani daga cikinsu ya hau kujerar gwamnan Jihar ba (duk da i'kirarin da suke yi cewa sun fi ko wacce 'kabila yawan mutane a Jihar). Wannan ne ya sa yayin da sauran 'yan siyasa su kan tauna su kuma ciza magana kafin su furta, shi Jang ko yaya ta zo furzarwa ya ke—komai munin ta.
Wasu majiyoyi sun ruwaito cewa a lokacin da yake neman tsayawa takarar gwamna, al’ummar Musulmi sun nemi ya za'bo mataimaki Musulmi don su goya masa baya. Shi kuwa sai ya ka da baki ya ce shi bai ga dalilin da zai sa ya d'auki mataimaki Musulmi ba, don kuwa yana ganin Musulmi ba su da wani tasiri ko muhimmanci a tsarin rayuwar Jihar Filato: ma’ana, da su da babu su duk d'aya ne a wurinsa, kai idan akwai yadda zai yi ya kawar da su ma zai yi. Mutanen Jihar Adamawa, inda ya ta'ba yin Gwamnan mulkin soja, ma sun shaidar da cewa ba ya 'kaunar Musulunci da Musulmi.
Bayan wannan, tun bayan hawansa gadon mulki a Jihar Filato, Jang ya ke ta d'aukar matakai da za su iya yin karen-tsaye ga gurguntaccen zaman lafiyar da yake wanzuwa a Jos tun bayan rikicin 2001. Misali, jajircewar da ya yi sai ya d'auke Sakatariyar 'Karamar Hukumar Jos ta Arewa daga inda ta ke ya kai ta inda 'yan 'kabilarsa ta Birom su ka yi dafifi, duk kuwa da cewa wancan wurin yana da nisa daga cibiyar garin Jos, kuma su 'yan 'kabilar tasa ba su taka kara sun karya ba a 'karamar hukumar. Sannan kuma ya nace sai ya fad'ad'a fadar Gbong Gwom Jos, ya gina masa majami'a, duk kuwa da cewa shi Sarkin Birom d'in bai ta'ba kwana a fadar ba. Kai ko Fom Bot ma bai ta'ba kwana a fadar ba, balle Victor Pam.
Idan ba a manta ba, a za'ben da ya soke kwanan baya, Jang ya d'auki duk wasu matakai da ya ke ganin za su bashi dama ya d'ora d'an uwansa a kan karagar shugabancin 'Karamar Hukumar Jos ta Arewa amma bai yi nasara ba. Don haka a wannan karon, kamar yadda wasu majiyoyi su ka ruwaito, ya 'kalubalanci wasu 'yan barandansa daga cikin al’ummar garin Jos da ko da yaya su tabbata su kawo masa 'karamar hukumar. Wad'annan 'yan barandan nasa su ne su ka d'auki nauyin wasu zauna-gari banza, da kuma 'yan bunburutu don su ri'ka kafewa da kuma gadin fastocin d'an takarar Jang a cikin garin Jos. Sannan kuma, kamar yadda wad'nnan majiyoyi su ka ruwaito, aka umarci wad'annan tsagera su tayar da yamutsi idan su ka ga d'an takarar Jang ba zai yi nasara ba.
Bayan Jang ya haddasa zanga-zanga, nan da nan ya umurci 'yan sanda su bud'e wuta a kan duk wanda su ka gani. Abin mamaki shine duk da cewa mutanen Jos gaba d'aya sun shige cikin gidajensu bayan jin wannan umurni da aka bayar ga 'yan sanda, sai ga 'yan sandan kwantar (wad'annan tayarwa su ka yi ta yi) da tarzoma suna bi gida gida suna fasa 'kofa su na kashe bayin Allah da ba su ji ba, ba su gani ba. Wasu ma na cewa 'yan CAN (wato 'Kungiyar Kiristoci ta Nijeriya) ne sanye da kayan 'yan sanda ke kashe mutane—in ma hakan ne to ba abin mamaki ne, don tun farkon shekarun 1990 jaridar The Pen, wacce ta dad'e da kwanta dama, ta ruwaito cewa 'kungiyar na ta tara muggan makamai don kai hari a kan Musulmi.
Sannan kuma Gwamnatin ta bayar da labarai ga kafofin yad'a labarai na kudancin Nijeriya mai nuna cewa al’ummar Musulmi ne su ka ri'ka kashe mutane. Ka ga ke nan an cuci mutane an kuma d'ora masu laifi. Ga wanda bai sani ba, wakilan wad'annan kafofin watsa labarai na kudu a zaune su ke ko yaushe a gidan gwamnati, idan labari ya zo su kar'ba a biya su su aika don jaridunsu su buga. Na ma ta'ba zuwa wani gidan gwamnati inda na ga irin wad'annan 'yan jarida suna fad'a a wajen rabon irin kud'in da ake ba su. Shi yasa duk jaridar da ka karanta sai ka ga labarin ya sa'ba da ha'ki'kanin abin da yake faruwa — me zai hana kuwa, tun da labarin daga Nuhu Gagara aka samo shi?
Babu shakka Jang shi ke da alhakin kashe d'aruruwan mutane a Jos saboda tsabar 'kiyayya da kafiya a kan abin da bai dace ba — abin da mai hankali da tunani da hangen nesa ba zai yi ba. Idan burin Jang da sauran ma'kiya Allah shi ne su kawar da Musulmi a garin Jos, to fa ya kamata su san cewa ba za su iya aiwatar da abin da Allah bai yi ba. Sannan kuma ya kamata su fahimci cewa akwai ranar 'kin dillanci.
Kuma yana da kyau Jang ya gane cewa idan har ya dage a kan aiwatar da wad'annan munanan manufofi nasa, to zai kai garin Jos da ma Jihar Filato ya baro ne kawai. Ga misali nan wad'anda su ka san garin Langtang suna bayarwa: rikicin da ya hautsina garin ya mayar da shi kangon garin da aka sani a da. To ko da su Jang sun samu damar kashe dukkan Musulmin da ke Jos, to fa garin ba zai ta'ba farfad'owa har su su ji dad'in zama a cikinsa ba.
Dangane da tunaninsa na cewa Musulmi ba su da tasiri kuwa, ya kamata ya tuna da 'kauracewa harkokin da al’ummar Jos su ka yi wanda ya tsayar da dukkan al’amura a garin. Wannan yana nuna cewa muddin al’umma ta 'kauracewa garin to ya mutu ke nan murus.
Su kuwa al’ummar garin Jos, ya kamata su san cewa lokaci ya yi da ya kamata su koma su sake shiri. Abin nufi a nan shi ne su sake tsarin tafiya. Babu shakka al’umma, musamman shugabanni, yanzu sun gane kurensu, musamman wajen za'ben d'an majalisar Jiha mai wakiltar Jos ta Arewa wanda ba shi da hadafi, bai san ciwon kansa ba. Kuma lokaci ya yi da ya kamata a had'a kai a fara d'aukar tsauraran matakai a kan mutanen da ake had'a baki da su don a cutar da al’umma. Me zai hana a sanyawa irin wad'annan mutanen irin takunkumin da aka sanyawa sahabban da su ka 'ki fita ya'ki a zamanin Manzon Allah (Tsira da Amincin Allah su tabbata a gareshi)?
Ita kuma Gwamnati, musamman ta tarayya, wajibi ta yi bincike don gano musabbabin wannan rikici, ta kuma hukunta duk wanda aka same shi da laifi. Hukuncin kuma kar ya tsaya a kan wand'anda su ka d'auki makamai kawai, wajibi ne ya had'a har da wad'anda suka bayar da umarni da baki, da wad'anda su ka shirya magud'i. Kai ire-iren maganganun da ke fitowa daga bakin wad'annan mutane ma ya kai a d'auke shi a matsayin cin amanar 'kasa. Misali, wanne sashe ne na Kundin Tsarin Mulkin Najaeriya ya ce sai 'yan wata 'kabila ko addini ne kawai za su shugabanci wata 'karamar hukuma; har ta kai ga tsara yadda za a karkashe mutane don cimma wannan buri?
Allah Ya ji'kan Musulmin da suka rasa rayukansu a wannan aika-aika da Jang ya aikata; shi kuma Allah Ya nuna masa iyakarsa. Allah Ya taimaki Musulunci da Musulmi, amin.