Friday, January 25, 2008

Shin Me Jang Yake Nufi da Jos?


Alamu na nuna cewa duk wata gwamnati da ta kafu a Jihar Filato tana zuwa da wasu manufofi na musamman dangane da garin Jos da kuma 'Karamar Hukumar Jos ta Arewa. Wannan, ko shakka babu, ba zai rasa nasaba da kasancewar wannan wuri cibiyar mulki da hada-hada ta Jihar ba. Amma babu gwamnatin da ta zo da d'amsul basirati, da rashin hangen nesa, da kuma tsananin d'imuwa kamar gwamnatin Jang.
Da farko dai, kasancewa tun bayan kafa Jihar ba a ta'ba samun d'an 'kabilar Birom d'in da aka za'ba don ya mulke ta ba, wannan gwamnati, ga alama, ta zo da burin ganin ta tabbatar da duga-dugan ‘yan 'kabilar Birom a kan madafun iko a Jihar. Kwanan nan wani mai baiwa tsohon gwamna Joshua Dariye shawara ya koka cewa Gwamna Jang ya kori wasu jami’ai ya maye gurbinsu da ‘yan wata 'kabila guda d'aya.
A irin wannan yun'kuri, wata'kila Jang yana so ne ya ga cewa mutanensa sun kame Jos, kamun kazar kuku, domin wannan zai taimaka musu wajen yin yadda suka so da Jihar, duk da cewa ‘yan 'kabilar Birom d'in da ke 'Karamar Hukumar Jos ta Arewa ba su taka kara sun karya ba. Wannan dalili ne ya sa ya ke so ya fad'ad'a fadar Gbong Gwom Jos, bayan ya tashi Sakatariyar 'Karamar Hukumar Jos ta Arewa daga inda take. Kamar yadda wata majiya ta ruwaito har ma katafariyar majami’a (coci) wadda babu irinta a 'kasar nan za a gina a wurin.
Abu na biyu kuma shine 'kir'kirar wasu 'kugiyoyin shara da aka yi ba tare da tuntu'bar al'ummar gari ba, aka wakkala musu bi unguwa-unguwa a garin Jos don kwashe shara, a 'karshen mako kuma su kar'bi wasu kud'ad'e daga hannun jama’a. yawancin kwandunan sharar da wad'annan mutane suka ajiye a wuraren kasuwanci ne inda kud'i ke shiga da fita ba 'ka'k'kautawa. To amma bayan ba su kwashe ko da tsinken tsintsiya a wad'annan wurare ba, sai ga masu kwasar shara sun zo kwasar kud'i. Ci-ma-zaune ke nan!
Haka zalika, wannan gwamnati ta 'kir'kiri wani haraji na babu gaira babu dalili wai shi harajin zaman gari (tenancy rate). Amma na ji hatta tsirarun ‘yan 'kabilar Birom d'in da abin ya rutsa da su suna tofin Allah-tsine; ko da yake ba don su aka yi wannan doka ba.
Baya ga wannan, kwatsam sai gwmnatin Jang tace wai za ta hana yin a-ca'ba a cikin garin Jos da kuma 'Bukur! Jin haka ke da wuya mutane suka fara cewa ai wannan ba wani abu bane illa yun'kurin hanawa wasu jama’a sana’ar da za su yi su ci abinci. A 'kiyasin shugaban ‘yan a-ca'ba na Jihar, dubban mutane ne, yawancinsu matasa, za su shiga halin ni-‘ya-su idan hakan ya tabbata.
Ko da ya ke daga baya gwamnatin ta zo da bayanin cewa Kwamishinan Muhalli da Raya Birane na Jihar, wanda shi ne ya yi waccan maganar, ba da yawun gwamnati ya yi ta ba, masu iya magana sun ce wai “idan ka ga kare yana sansana takalmi to d'auka zai yi. Ma’ana, babu wani kwamishina da zai zo ya yi magana ta 'kashin kansa a kafofin yad'a labarai ba tare da ya fayyace cewa wannan magana ra’ayinsa ce ba, sannan kuma ya ci gaba da ri'ke mu'kaminsa.
Da ma can an ta'ba rad'e-rad'in cewa Majalisar Dokoki ta Jihar Filato ta yi yun'kurin hana aca'ba amma ta fasa saboda idan ta yi hakan ‘yan aca'ba da yawa za su koma makaranta. To idan gwamnatin Jang ta yi nasarar hana aca'ba, wasu daga cikin ‘yan aca'ba za su koma makarantu don 'karo ilimi, wasu kuwa makarantun ashsha za su shiga. Ma’ana wad'anda ba za su iya komawa makaranta ba, babu shakka za su shiga sace-sace ne, da aikata sauran laifuffuka. Wata'kila sannan Jang zai yi 'ko'karin magance wannan matsala ta hanyar sanyawa a karkashe su. Don dama manufar it ce a kore su daga garin 'karfi da yaji.
Dukkan yun'kurin da aka yi a baya na ganin an karya wannan al’umma ya 'ki yin tasiri. Baya ga 'kona kasuwar Jos da gangan don ganin an talauta su, an 'ki sake gina ta da gangan. To amma a maimakon su karye, sai 'kara bun'kasa su ke yi, Allah Yana 'kara musu arzi'ki da wadata. Dama Hausawa sun ce, “Wani hanin ga Allah baiwa ne”.
Idan ba a manta ba, lokacin da ya tsaya takara a 'kar'kashin jam’iyyar ANPP a shekarar 2003, Jang ya yi al'kawarin zai sake gina Babbar Kasuwar Jos. Ya yi wannan al'kawarin ne lokacin da ya je ya'kin neman za'be a 'Karamar Hukumar Jos ta Arewa, sanin cewa mafi yawan mutanen da ke da rumfuna a kasuwar mutanen 'Karamar Hukumar ne. Amma yanzu sai ga shi Gwamnan ya nuna cewa ba zai sake gina kasuwar ba, duk da cewa lokacin dokar ta 'baci Kantoman Jihar, Kanar Kiris Alli mai ritaya ya ma bayar da kwangilar sake ginin. A maimakon haka Jang nema ya ke ya tursasa mutane su koma wani fa'ko wanda ya ke nesa da idon jama’a; hala bai ta'ba jin wa'kar Marigayi Alhaji Mamman Shata ba inda ya ke cewa: “Yawan mutane shi ne kasuwa, ni ku raba ni da tarin rumfuna”.
Abin 'karin ban haushi ma shi ne rad'e-rad'in cewa Jang yana nema ya tashi mutanen da ke 'Karamar Kasuwar Jos wadda aka fi sani da suna “New Market”—inda ‘yan kasuwa da d'an dama suka koma suka tsuguna bayan tarwtsa Babbar Kasuwa. A maimakon kasuwar, wai Jang so ya ke yi ya gina dandalin sha'katawa. To Allah Ya sa wannan labari ya 'kare a jita-jita; don in ba haka ba, kusan dukkan abubuwan da Jang ya ke shiryawa za su zama abin da bature ya ke cewa “To cut the nose in order to spite the face”, ma’ana, a garin neman gira za a rasa ido.
Yana da kyau a fahimci cewa tarihi ya nuna babu wata 'kasa ko al’umma da za ta ci gaba ita kad'ai ba tare da cud'anya da mu’amala da wasu wad'anda ta ke ganin bare ne ba. Duk wata wayewa a tarihin duniya sakamakon musayar ra’ayi ne da cud'anya a tsakanin al’ummu daban-daban. Ko ci gaban da a ke ganin Amurka—'kasar da a ke ta han'koron kwaikwayo a wannan zamanin—ta yi, had'uwar al’ummu da dama ne ya kawo shi. Ko a nan Nijeriya ma, garuruwan da suka bun’kasa ta fuskar kasuwanci ko masana’antu, ko ma siyasa, irin su Legas, Kano, da sauransu, za ka samu cewa tare da taimakon al’ummun da suka taso daga wasu wurare suka bun’kasa.