Monday, March 24, 2008

'Yar'aduwa A Taron OIC: Ihu Bayan Hari

Duk mai lura da al’amuran yau da kullum ya san cewa Kungiyar Kiristoci ta Nijeriya (Christian Association of Nigeria [CAN]) a koyaushe tana nuna 'kiyayyarta a fili ga duk wani abu da ya shafi Musulmi ko Musulunci, ko da kuwa wannan abin yana da amfani ga al’umma. Don haka ba abin mamaki ba ne idan 'Kungiyar ta yi suka ga halartar Malam Umaru ’Yar’aduwa taron 'kasashen Musulmi da aka yi a Senegal. Abin mamaki, a gani na, shi ne da ’Yar’aduwa ya ma halarci taron.
A watan Janairun wannan shekara, Sakatare-Janar na 'Kungiyar 'Kasashen Musulmi (Organisation of Islamic Conference [OIC]), Farfesa Ekmeleddin Ihsanoglu, ya kawo ziyara Nijeriya. Kafin ya zo 'kasar kuwa sai da ya biya ta wasu 'kasashen Afirka.
Kamar yadda manema labarai suka ruwaito, Ihsanoglu ya zo Nijeriya ne don ganawa da jami'an gwamnati, da Sarkin Kano, da kuma Sarkin Musulmi dangane da rawar da OIC za ta taka wajen kawar da talauci da cututtuka a Nijeriya. Amma abin ba'kin ciki, haka wannan babban ba'ko, wanda ya taho da kyakkyawan nufi, ya koma ba tare da ya samu ganin wad'annan jami'ai ba.
Kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito, yayin da Sarkin Kano ba ya 'kasar lokacin da jami'in OIC d'in ya zo, Fadar Sarkin ta bayyana cewa ba su da labarin zuwan Ihsanoglu. Makamancin wannan bayani ne ya fito daga Fadar Sarkin Musulmi a Sakkwato. Sai dai shi Ihsanoglu ya tabbatar da cewa tun kafin ya taso daga Hedikwatar OIC, jami'an ofishin jakadanci na 'kasarsa, Turkiyya, sun tabbatar masa sun tuntu'bi jami'an Nijeriya wad'anda suka tabbatar masu cewa komai ya kammala don kar'bar wannan babban ba'ko.
Amma abin takaici, sai ga shi yayin da a sauran 'kasashen da ya ziyarta Ministocin Harkokin Waje ke tarbar Sakataren na OIC, sannan daga bisani ya gana da Shugabannin wad'ancan 'kasashe. Amma a Nijeriya, sai wani permanent sakatare a Ma'aikatar Harkokin Waje aka tura ya taro Ihsanoglu. Duk da cewa Ministan Harkokin Waje ba Musulmi ba ne, to ya kamata a ce ya tura d'aya daga cikin 'Kananan Ministocinsa (wanda Musulmi ne). Amma da ya ke ba su d'auki Ihsanoglu da muhimmanci ba ba a yi hakan ba.
Ba kuma za mu manta da cewa bayan Ihsanoglu ya bar 'kasar nan ba tare da ganin 'Yar'aduwa ba, jami'an kamfanin Siemens, kamfanin da aka zarga da bayar da ma'kudan kud'ad'e cin hanci ga wasu manyan jami'an Nijeriya sun kawo ziyara, kuma 'Yar'aduwa ya tarbe su a Aso Rock Villa, yana mai annashuwa da sakin fuska. Wannan ya nuna cewa wula'kancin da aka yiwa Ihsanoglu da gangan aka yi; saboda shi ba d'an jari-hujjan Yammacin duniya ba ne.
Don haka na ke ganin wad'anda ke jan akalar Gwamnatin 'Yar'aduwa - wata'kila - ba da son ransu ya halarci taron OIC ba. Babu mamaki sune suka zugo CAN ta fad'i abin da ta fad'a duk da cewa surutai ne kawai marasa tushe bare makama.

Saturday, March 15, 2008

Jakin Dawa Ya Ga Na Gida

Allah wadaran naka ya lalace, wai jakin dawa ya ga na gida.

Ya zuwa yanzu dai ya kamata a ce mugun 'bacin ran da hukuncin Kotun Saurarar 'Karar Za'ben Shugaban 'Kasa da aka a watan Afrilun bara ta yanke ya fara yayewa. Amma ba'kin cikin da wannan al'amari ya haifar abu ne wanda za a dad'e yana zogi a zukatan mafi yawan 'yan Nijeriya.
Kowa dai ya ji yadda wannan kotu, babu kunya bare tsoron Allah ta yi fata-fata da dukkan hujjojin da aka gabatar a gabanta, alhali kuma, kamar yadda lauyan Janar Muhammadu Buhari ya zayyana, ta ma hana a gabatar da wasu shaidun 'kwarara. Abin da ya fi komai 'kuna shi ne yadda wannan kotu ta wanke Shugaban Hukumar Za'be, Maurice Iwu daga duk wani laifi, alhalin ko shi kansa Malam Umaru ya fad'a da bakinsa cewa an tafka aika-aika a wannan za'be.
To dama dai mutane da yawa sun ce "a rina" (wai an saci zanin mahaukaciya) lokacin da labari ya bayyana cewa Malam Umaru ya gabatar da sunan shugaban wannan kotu a gaban Majlisar Dattijai don a masa 'karin girma zuwa Koyun 'Koli ta 'Kasa. Wasu sun nuna cewa wannan al'amari tsautsayi ne don kuwa ba Malam Umaru ba ne ya za'bo Ogebe. Amma abin da wa'kila mutane ba su yi la'kari da shi ba shine al'amarin nan fa a wajen PDP na ko-a-mutu-ko-a-yi-rai ne. Me zai hana PDP ta yi amfani da wasu mutane a Hukumar Kula da Harkokin Shari'a ta 'Kasa (National Judicial Commission [NJC]) wajen ganin an mi'ka wad'annan sunaye a daidai lokacin da ya dace?
A halin da ake ciki yanzu dai, Majalisar Dattawa ta tabbatar da cicci'ba Ogebe zuwa Kotun 'Koli. Sai dai rahotanni suna nuna cewa lokacin da aka zo mi'ka sunayen mutum biyu don cike gurbin da ke Kotun 'Kolin akwai wani jajin da shi ma ya cancanci tafiya amma ya janye don baiwa Ogebe dama. Haka zalika rahotanni na dad'a nuna cewa lokacin da ake muhawara a Majalisar Sanatoci, wani Sanata ya nuna cewa idan aka bi 'ka'idar cika gurabu bai kamata Ogebe ya je Kotun 'Koli ba saboda tuni Jihar da ya fito, wato Binuwai, tana da wakilcin Mai Shari'a Katsina-Alu, amma sanatocin suka yi watsi da wannan mulahaza.
Wasu rad'e-rad'i da ke kewayawa a Abuja bayan yanke wancan hukunci na cewa da farko ba duka alkalan kotun ne ma suka goyi bayan wancan d'anyen hukuncin ba. A cewar wad'annan rad'e-rad'e ta hanyar matar d'aya daga cikin al'kalan aka bi aka sauya masa ra'ayi.
Idan dai aka je aka zo, ko ma dai yaya aka yi, wannan hukunci da Ogebe ya jagoranci yankewa ya tabbatar da abu d'aya: duk magud'in za'ben da za a tafka a 'kasar nan, komai muninsa, ba laifi ba ne a dokar 'kasa. Don haka a gaba kowa sai ya zage, ya zage damtse ya tafka iyaka iyawarsa: duk wanda ya ci ya sha wanda ya tsaya gaskiya kuwa, to sai dai ya yi Allah Ya isa. Ba shakka kuwa Allah isashshe ne, kuma idan ba ba ji kunya a duniya ba, to tabbas za a ji ta a Lahira.