Saturday, May 17, 2008

"Mun 'Daura 'Damarar Ya'ki Da Jahilci Da Zaman Banza"


Daga Muhammad K. Muhammad
Alhaji Lawan Alhassan Mai Warwaro shi ne shugaban ri'ko na 'kungiyar Ibrahim Katsina Foundation (wato 'Kungiyar Raya Unguwar Ibrahim Katsina) da ke 'Karamar Hukumar Jos ta Arewa. A wannan hirar da ya yi da Aminiya ya bayyana manufofin kafa 'kungiyar da kuma nasarorin da ta samu ya zuwa yanzu.
Aminiya: Menene ma'kasudin kafa wannan 'kungiya ta Ibrahim Katsina Foundation?
Alhaji Lawan: Dalilan da suka sa muka taru muka yi tunanin kafa wannan 'kungiya suna da dama 'kwarai. Kai da kan ka in ka lura [za ka ga] kullum duniyar ta mu 'kara ci gaba ta ke yi. Kuma ci gaba ba ya yiwuwa sai da al’umma; kuma ba ya yiwuwa da al’ummar sai an had'a kai. Duk sanda al’umma ta had'a kai, to za ta ci nasara a kan dukkan abin da ta sa a gaban ta. Amma daga lokacin da aka samu al’umma a d'aid'aikun su a warwatse, to karya su ba shi da wahala.
In ka lura, mu al’ummar mu ba mu saba da irin wad'annan 'kungiyoyi ba. 'Yan uwan mu da suke kudu ko yamma sun dad'e suna irin wad'annan tafiyoyin. Amma kuma daga lokacin da muka fara zuwa yanzu, mun yi 'karfin da 'kungiyoyin da suka shekara 50 ma ba su yi ba.
Aminiya: Ko za ka iya fad'a mana kad'an daga cikin manufofin wannan 'kungiya?
Alhaji Lawan: Manufar wannan 'kungiya ita ce: 'karfafa al’umma a kan al’amura, kamar ta wajen ilimi, ayyukan yi, dogaro da kai, wayar wa da mutane kai su san cewa su mutane ne—su san ’yancin kan su, zaman lafiya, da sauransu.
Aminiya: To wad'anne irin nasarori ku ka samu daga lokacin da aka kafa wannan 'kungiyar zuwa yanzu?
Alhaji Lawan: Alhamdulillahi, mun samu nasarori da dama. Na d'aya daga cikin abubuwan da muka fara yi, mun fara duba menene ya kan sa al’umma ta ci baya ko ta kasa ci gaba? Sai muka gane jahilci ne. Idan babu ilimi babu inda za a je. To sai muka ce mu fara d'aukar maganar ilimi mu sa a gaban mu. Sai muka duba al’ummar don mu ga ta ina ne za mu fara taimakawa ta 'bangaren ilimi? Sai muka ga akwai yara 'kanana wad'anda ba su zuwa makaranta, suna nan sai zaman banza, sai yawace-yawace. Sai muka kafa kwamiti mu ka ce ya binciko mana irin wad'annan yara, musamman marayu, da wad'anda iyayen su ba su da hali, amma suna da basirar karatu. Mu ka samu sunaye da dama daga ko wanne 'bangare na wannan maza'ba.
A wancan lokacin mun fara da yara kamar guda 40; muka sa su a firamare, muka biya masu kud'in makaranta, muka d'inka masu kayan makaranta, muka saya masu littattafai, kuma muka kafa kwamitin sa-ido (monitoring team) wanda ya ke zuwa makarantun nan ya tabbatar yaran nan suna zuwa kuma suna yin abin da ya kamata. 'Bangare na farko ke nan.
'Bangare na biyu shi ne sakandare. A wannan 'bangaren mun duba mun ga akwai yaran mu da yawa da suka gama firamare; su ma suna da bu'katar ci gaba amma babu hali. Muka taru muka yi doguwar shawara, muka ce akwai makarantu na ’yan uwa da abokan arzi'ki a gari wad'anda idan muka je muka ro'ki alfarma za a yi mana; saboda haka sai muka fara da makarantar uban mu, Alhaji Barau Abdullahi, mai suna Al-Hilal. Allah Ya taimake mu muka samu gurbin yara 10, wad'anda aka ba su daga 'karamin aji na d'aya (JSS1) har zuwa babban aji na uku (SSS3). Wato ba abin da za a biya a makarantar nan—su gudummawar su ga wannan 'kungiya ke nan.
Daga nan kuma sai muka tafi wata makaranta da ake kiran ta Trust International, ta Alhaji Tijjani Abdullahi. Nan ma—ko da yake ya ce shi ma akwai yaran marayu da ya ke taimaka wa da dama, amma tun da manufar mu ta alheri ce—ya ba mu [gurbin] mutum biyu.
Daga nan kuma sai muka tafi wajen wani d'an uwan mu Alhaji Hamisu Umaru, shi ma yana da makaranta mai suna Al-Haqq. Shi ma ya ba mu gurabe biyu. Sai kuma wani d'an uwan mu, Malam Idi Abubakar, yana da makaranta mai suna Al-Ikhlas. Shi ma ya yi mana alfarma, ya ba mu gurabe biyu. Dukka wad'annan su na nan a makarantun suna karatu.
Bayan waxannan kuma akwai wad'anda mu ke ta bi da dama, suka ga lokaci ya 'kure; amma bayan zangon karatu na ukun nan (third term), in Allah Ya yarda za mu samu gurabe da dama da za mu 'kara tura yara. Sannan a makarantun gwamnati ma muna nan muna 'ko'karin mu sa yara kamar guda 40. Mun tura ana ta yi mana 'ko'karin sama masu admission. Wannan 'kungiya ce za ta nemo kud'i ta biya masu kud'in makaranta, ta d'inka masu kayan makaranta, ta saya masu littattafai. Mu dai burin mu mu ga mun kawar da zaman banza, da jahilci da yaran mu ke yi.
Sannan muna da kusan mutm 50 masu bu'katar yin digiri. To suma mun bi jami’o’i kamar guda uku muna 'ko'karin cusa su. Sannan muna da wani uba, Malam Musa Muhammad, Limamin Abuja, shi ma ya d'ebi yara uku ya ba su tallafin karatu (scholarship) daga sakandare har zuwa jami’a—banda wad'anda na yi bayaninsu—Allah Ya saka mishi da alheri.
Akwai kuma yaran da suka gama karatu amma babu aikin yi. To su muna da ’yan uwa irin su Jalalu Arabi da Alhaji Umaru Sani, wad'anda su ke 'ko'karin taimakawa wajen sama masu aiki. Ta 'bangaren sana’o’i kuma muna da burin taimakawa; a hankali muna nan muna tunanin yadda duk jama’ar unguwa har ma da matan aure, za su amfana.
Sannan akwai wasu yara masu shaye-shaye, da ’yan sara-suka. Su kuma mun je mun samu Hukumar Ya'ki Da Mu’amala Da Miyagun 'Kwayoyi, NDLEA, da DPO na ’yan sanda don su ba mu gudmmawa don mu tabbatar mun kawar da wad'annan abubuwa daga wannan unguwa tamu. Yanzu haka ma shirin da mu ke yi za mu je mu gana da kwamishinan ’yan sanda don mu had'a kai mu tabbata al’umma ta zauna lafiya. Kuma muna 'ko'karin ganin idan rashin fahimta ya faru a unguwa tsakanin mutum da mutum, to kar a yi saurin zuwa wajen hukuma: a kawo wajen wannan 'kungiya in Allah Ya yarda za ta tabbatar ta sulhunta. Wad'annan kad'an ke nan daga cikin nasarorin da mu ka samu.
Aminiya: Babu shakka ana bu'katar kud'i don gudanar da dukkan wad'annan abubuwa da ka fad'a. Wad'anne hanyoyi wannan 'kungiya ta ke bi don samun kud'in da ta ke gudanar da ayyukan ta?
Alhaji Lawan: A yanzu dai 'kungiya ta na samun kud'in ta ne a tsakanin ’yan 'kungiya. Da farko, mun sanya cewa ko wanne mamba zai bayar da a'kalla naira 50 ko wanne wata. A cikin mu kuma, akwai wad'anda Allah Ya fifita su, wad'anda in wani abu ya taso za mu je wajen su, su cire abin da ke aljihun su a cikin arzi'kin da Allah Ya ba su su ce a je a yi.
Wannan abu da mu ke ta yi duka a jikin mu ne. Mu ya mu ne mu ke ta 'ko'karin samo wannan kud'i. Lokacin da muka fara wannan al’amari, mun fara ne da neman taimakon motar d'aukan gawa. To a wancan lokacin mun samu kud'i isassu, mun sayi wannan mota tana nan tana aiki. To kud'in da suka saura a wancan lokacin su ne su ka zama tsanin da muka taka mu ka fara yin wad'annan ayyuka.
Wad'annan ’yan hanyoyi su ne 'kungiyar nan ta ke bi a yanzu ta ke samun kud'i, amma nan gaba za ta fad'ad'a su in Allah Ya yarda.
Aminiya: Akwai wani taimako ne da ku ke samu daga gwamnati da kuma sauran jama’ar gari?
Alhaji Lawan: Ba mu fara tuntu'bar gwamnati ba tukuna; domin da muka fara 'kungiyar ba ta da kundin tsarin mulki (constitution), sai daga bayan nan muka samu. Yanzu muna 'ko'karin samun rajista ne a hukumar rajistar kamfanoni (CAC). Idan muka samo wannan rajista to mun samu sanda da za mu je gaban gwamnati mu nuna mata 'kungiyar ta kafu ta zauna da gindin ta. In Allah Ya yarda muna kan wannan.
Aminiya: A 'karshe wanne irin kira za ka yi ga al’ummar unguwa don su bayar da had'in kai ga wannan 'kungiya?
Alhaji Lawan: Ina kira ga al’ummar unguwa gaba d'aya su juyo hankalin su su ba wannan 'kungiya had'in kai. Wannan 'kungiya wacce idan suka dube ta da kyau za su ga cewa a duk garin nan ko Jihar nan, babu 'kungiyar da ta ke da manufa da niyya mai kyau kamar ta. Kuma 'kungiyar ta taso a d'an 'kan'kanin lokaci, ta ci nasarori da daman gaske. Saboda haka ina kira ga dukkan al’ummar wannan unguwa su ba wannan 'kungiya goyon baya; duk lokacin da ta kira su su amsa, duk lokacin da ta nemi gudummawar su ko wacce iri ce su bayar. Ba ma mutanen unguwa kawai ba; ina kira ga mutanen gari ne gaba d'aya. Yanzu misali mu na wa garin mu addu’a da ’ya’yayen mu, da kuma addu’ar zaman lafiya. Duk 'karshen wata mu kan taru a d'aya daga cikin masallatan unguwar mu, mu sauke Al-'Kur’ani, mu yi sadaka, mu yi addu’o’i Allah Ya zaunar da mu lafiya: Allah Ya zaunar da garin mu, da Jihar mu, da 'kasar mu lafiya. Kuma ’ya’yayen mu Allah Ya shiryar da su Ya ba su ilimi mai albarka.
Jaridar Aminiya, 11 ga Jumada Ula, 1429 (16 ga Mayu, 2008)

Tuesday, May 06, 2008

Gargad'i Ga Mata

Daga Muhammad K. Muhammad
Sharhin littafin Mu Yi Hattara Mata wanda Maryam Tsoho Mai Doya ta rubuta; Yawan Shafuka: 78; Shekarar wallafa: 2007
Sakamakon wasu rubuce-rubuce da masana irin su Rabaran Thomas Malthus suka yi, wad'anda ke nuna cewa 'karuwar al’umma ya zarta abin da albarkatun da ke duniya za su iya d'auka, 'kasashen Yammacin duniya suka cusa a'kidar rage yawan haihuwa ko ma gudun ta gaba d'aya a zukatan al’ummar su. Irin wannan a'kida ita ce ta yad'u har zuwa 'kasashen Musulmi, inda aka samu wasu, musamman ’yan boko, suka ara suka yafa, duk kuwa da cewa wannan tunani ya sa'ba da karantarwar Musulunci.
A 'ko'karin su na rage haihuwa ko ma guje mata kacokan, wad'annan mutane su kan tilasta matan su na aure shan magungunan hana daukar ciki; idan magungunan ba su yi nasara ba kuma, su kai su a zubar da abin da aka samu. Dalilan su kuwa ba sa wuce tsoron talauci, ko gudun d'aukar nauyi (a ganinsu) da son more rayuwa. Wannan al’amari shi ne ya tayar da hankalin Maryam Tsoho Mai Doya, ta yanke shawarar ta rubuta littafi don gargad'in mata da kuma yin tir da halayen maza masu aikata wannan aika-aika.
Tun tashin farko marubuciyar ta yi shimfid'a da bayar da labarin abin takaicin da ya dame ta har ya kai ta ga tunanin rubuta wannan littafin. A nan ne kuma mallamar ta shaida wa mai karatu cewa idan ana maganar illar matakan hana d'aukar ciki wad'anda Turawa suka kawo, to ita ganau ce ba jiyau ba. Don kuwa ba don ta je asibiti don neman maganin illar da robar hana d'aukar ciki ta yi mata ba, to da ba ta had'u da wata baiwar Allah da ta ba ta tausayi ba.
Mallama Maryam ta had'u da wannan baiwar Allah ne a yayin da ta ke bin layin ganin likita. Ita wannan mata tana ta ajiyar zuciya, lokaci zuwa lokaci kuma tana fad'in “wannan masifa da me ta yi kama?” Daga bisani wannan baiwar Allah ta shaida wa marubuciyar cewa mijin ta baya son haihuwa; don haka sanda ta d'auki ciki ya nemi ta je a zubar da shi, amma da ta 'ki sai ya kamata da duka a cikin har sai da ta suma.
Mu Yi Hattara Mata ya dubi wannan matsala a addinance, sannan kuma ya dube ta a al’adance. Ko wanne daga cikin babi shida na littafin ya fara ne da ayar Al-'Kur’ani ko Hadisin Manzon Allah (SAW). Sannan ya yi nuni da cewa ko a hankali ma, wad'annan abubuwa ne da yawancin al’ummu ba su yarda da su ba, don kuwa kundin tsarin mulki a 'kasashe da yawa ya haramta zubar da ciki. A cewar ta saboda “irin munin da illar wannan d'anyen aiki ke jawowa rayuwar mace, kundin tsarin hukunta laifuffuka na 'kasa, wato Penal Code, a sashe na 232(89) ya tanadi hukunci mai tsanani ga duk wanda ya zubar da cikin wata mace da ganagan, ba da wani dalili na ceton rai ba”.
Littafin ya kuma yi tsokaci game da illolin zubar da ciki wad'anda suka had'a da hujewar mahaifa, da hujewar mara, da kuma zubar jini. Mallamar ta kuma bayyana cewa idan aka samu kuskure wajen cire ciki ba a fitar da dukkan gudajin jinin da ke cikin ba, to wani cikin na iya tashi. Idan ma rashin sa’ar ya 'kara 'kamari, cikin ya kan tashi ne a wajen mahaifa.
Marubuciyar ta kafa hujja da Hadisin da ya ke cewa halittar d'an-Adam a cikin mahaifa na canjawa duk bayan kwana arba’in, da kuma bayanin masana kimiyya a kan halin da d'an tayi ya ke ciki a watanni taran da ya ke ciki, ta jaddada cewa duk wanda ya zubar da ciki bayan kwanaki 120 ya yi kisan kai, ya tozarta rai wanda Allah Ya ba shi ri'kon amana.
Don haka marubuciyar ta ke ganin cewa idan har ba a bu'katar cikin tun farko, bai kamata a yi gangancin d'aukar sa ba. A nan ne kuma ta yi dogon sharhi game da illolin hanyoyin hana d'aukar ciki da Turawa su ka kawo. Kamar yadda ta fad'a a farkon littafin, ta yi amfani da hanyar robar mahaifa wadda a kan sanya a mahaifa (IUCD); amma robar ta haifar mata da tsananin ciwon ciki da ya kai sai da aka yi mata aiki aka cire appendix. Sai dai wannan aiki bai magance ciwon cikin ba: bayan 'karin bincike wata likita ta zayyana wa marubuciyar illolin amfani da wannan roba wadda ta haifar mata da ciwon 'koda.
Marubuciyar ta kuma yi bayanin yadda 'kwayoyin had'iya ke toshe mahaifar mace su kuma samar mata da ciki “na gaibu” wanda a 'karshe ya kan jawo ciwon hanta da rashin sha’awa—wanda shi kuma ya ke haifar da matsala a tsakanin ma’aurata. Haka ma ta yi bayanin sauran hanyoyin hana d'aukar ciki da illolin ko wanne.
Amma marubuciyar ta kawo dalilan da za su iya halatta hana d'aukar ciki ko kawar da shi. Sai dai ta bu'kaci maza da a ko yaushe su tuntu'bi matan su kafin yanke shawarar abin da ya kamata su yi, don kuwa, a cewar ta, matan nan abokan zaman su ne ba bayi ba. Sannan ta kawo hanyoyi na al’ada wad'anda Shari’a ta yarda da su don hana d'aukar ciki wad'anda ba su da illa kamar azlu, shayarwa, hawa sama, da sauransu.
Yayin da marubuciyar ta ke kakkausan suka ga maza masu gudun haihuwa, ta yi sassauci matu'ka ga mata masu irin wannan ra’ayi, da ma wad'anda ke gudun haihuwa don tunanin za ta sanya masu saurin tsufa. Sai dai kuma za a iya tsammanin gargad'in da Mu Yi Hattara Mata ya yi a kan illar amfani da muggan hanyoyin hana d'aukar ciki da illolin zubar da shi zai zama hannunka mai sanda a gare su.
Jaridar Aminiya