Friday, December 14, 2007

JASAWA SUN BARA


Lokacin da Jasawa suka yanke shawara su 'ki fitowa aiki ko kasuwa don nun rashin jin dad'insu da abin da suka kira halin ko-in-kula da gwamnatin Jihar Filato take nunawa ga al'amuran da suka shafe su, abin ya baiwa kowa mamaki.
Hasali ma tasirin wannan ho'b'basa ya girgiza Jihar gaba d'aya, kama daga gwamnati har zuwa talakawa. Ba zato ba tsammani kawai aka wayi gari babu kowa a kasuwa babu wanda ya bud'e shago, babu motoci a tituna. A karon farko al'ummar Jasaw suka yanke shawarar d'aukar mataki kuma kowa ya bayar da had'in kai sa'banin yadda abin yake a can baya.
Daga cikin abubuwan da Jasawa suke adawa da su da suka sanya su d'aukar wannan mataki akwai yun'kurin da Gwmanan Jihar, Da David Jinah Jang ya ke yi an tshin sakatariyar 'Karamar Hukumar Jos ta Arewa daga inda take a yanzu ya mayar da ita ofishin Hukumar Tsabtace Garin Jos (Jos Metropolitan Development Board [JMDB]).
Al'ummar Jasaswa na ganin cewa d'auke sakariyar daga inda take a yanzu a mayar da ita wani waje mataki ne da gwmnatin ke 'ko'karin d'auka don nesanta su da harkar mulki a 'karamar hukumar kwata-kwata. Sanin kowa ne cewa wurin da sakatariyar take a yanzu wuri ne da Jasawa ke tin'kaho da shi a matsayin nasu-ko ba komai su kan ri'ka jin duk wani 'kwa'k'kwaran motsi da aka yi. Amma idan sakatariyar ta bar wajen shi ke nan sai a ri'ka yi babu su.
Dalili na biyu da ya sa Jasawa ba su amince da d'auke sakatariyar ba shi ne shirin da aka ce Gwmna Jang yana yi na gina wata 'kasaitacciyar majami'a a wurin da sakatariyar take. Hujjar Gwamnan ta yin hakan, kamar yadda wasu majiyoyi suka ruwaito, itace cewa a garuruwan sarakunan arewa za ka samu a kusa da fadar sarki akwai masallacin Juma'a. Don haka ya ke ganin ya kamata a ce a kusa da fadar Gbong Gwom (Sarkin Birom) wadda take kusa da sakatariyar akwai katafariyar majami'a.
Sai dai al'ummar gari suna gani rashin dacewar wannan hujja domin a cewarsu Gbong Gwom din nan, tun ma kafin rikicin da yayi kaca-kaca da garin Jos a shekarar 2001, ba ya kwana a wannan fadar. Saboda haka, a ganisu, akamta ya yi a tafi ko ma ina ya ke kwana a gina masa majami'a. Sannan kuma tarihi ya nuna cewa kusa da inda fadar Gbong Gwom d'in take, nan ne asalin fadar Sarkin Jos Isiyaku, wanda yake Bahaushe ne, kafin Turawan mulikin mallaka su kar'be sarautar su baiwa Rwang Pam. Bugu da 'kari kuma Jasawa suna ganin cewa tun da a yanzu 'yan 'kabilar Birom d'in da ke 'karamar hukumar Jos ta Arewa ba su da yawa, kamata yayi a d'auke fadar Gbong Gwom d'in gaba d'ayanta a mayar da ita inda mabiyansa ke da rinjaye.
Ko da yake wannan yajin fita da Jsawa suka yi ya yi matu'kar nasara da tasiri, an samu wasu balgurbi da suka nemi a yi wa al'amarin 'kafar ungulu. Daga cikinsu akawai wani wasu 'yan siyasa da suka shiga gari suna surutai suna sukar shugabannin al'umma. Wad'annan mutane, idan ab su yi a hankali ba, na fuskantar barazanar rasa samun kwanciyar hankali a tsakanin al'umma domin kuwa kowa na yi musu tofin Allah-tsine. A cikinsu akwai wanda aka ba shi wani mu'kami da ke da muhimmanci ga rayuwar ibadar Muslmi. Kuma wata majiya ta ruwaito cewa an bshi wannan mu'kami saboda an san cewa shi lalatacce ne, wanda zai iya had'a baki don cutar da al'ummarsa matu'kar zai samu d'an abin miya.
Hausawa dai na cewa "In rana ta fito tafin hannu bai iya kare ta" sannan kuma "Kowa ya daka rawar wani to tasa za ta 'baci". In kunne ya ji....