Monday, March 24, 2008

'Yar'aduwa A Taron OIC: Ihu Bayan Hari

Duk mai lura da al’amuran yau da kullum ya san cewa Kungiyar Kiristoci ta Nijeriya (Christian Association of Nigeria [CAN]) a koyaushe tana nuna 'kiyayyarta a fili ga duk wani abu da ya shafi Musulmi ko Musulunci, ko da kuwa wannan abin yana da amfani ga al’umma. Don haka ba abin mamaki ba ne idan 'Kungiyar ta yi suka ga halartar Malam Umaru ’Yar’aduwa taron 'kasashen Musulmi da aka yi a Senegal. Abin mamaki, a gani na, shi ne da ’Yar’aduwa ya ma halarci taron.
A watan Janairun wannan shekara, Sakatare-Janar na 'Kungiyar 'Kasashen Musulmi (Organisation of Islamic Conference [OIC]), Farfesa Ekmeleddin Ihsanoglu, ya kawo ziyara Nijeriya. Kafin ya zo 'kasar kuwa sai da ya biya ta wasu 'kasashen Afirka.
Kamar yadda manema labarai suka ruwaito, Ihsanoglu ya zo Nijeriya ne don ganawa da jami'an gwamnati, da Sarkin Kano, da kuma Sarkin Musulmi dangane da rawar da OIC za ta taka wajen kawar da talauci da cututtuka a Nijeriya. Amma abin ba'kin ciki, haka wannan babban ba'ko, wanda ya taho da kyakkyawan nufi, ya koma ba tare da ya samu ganin wad'annan jami'ai ba.
Kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito, yayin da Sarkin Kano ba ya 'kasar lokacin da jami'in OIC d'in ya zo, Fadar Sarkin ta bayyana cewa ba su da labarin zuwan Ihsanoglu. Makamancin wannan bayani ne ya fito daga Fadar Sarkin Musulmi a Sakkwato. Sai dai shi Ihsanoglu ya tabbatar da cewa tun kafin ya taso daga Hedikwatar OIC, jami'an ofishin jakadanci na 'kasarsa, Turkiyya, sun tabbatar masa sun tuntu'bi jami'an Nijeriya wad'anda suka tabbatar masu cewa komai ya kammala don kar'bar wannan babban ba'ko.
Amma abin takaici, sai ga shi yayin da a sauran 'kasashen da ya ziyarta Ministocin Harkokin Waje ke tarbar Sakataren na OIC, sannan daga bisani ya gana da Shugabannin wad'ancan 'kasashe. Amma a Nijeriya, sai wani permanent sakatare a Ma'aikatar Harkokin Waje aka tura ya taro Ihsanoglu. Duk da cewa Ministan Harkokin Waje ba Musulmi ba ne, to ya kamata a ce ya tura d'aya daga cikin 'Kananan Ministocinsa (wanda Musulmi ne). Amma da ya ke ba su d'auki Ihsanoglu da muhimmanci ba ba a yi hakan ba.
Ba kuma za mu manta da cewa bayan Ihsanoglu ya bar 'kasar nan ba tare da ganin 'Yar'aduwa ba, jami'an kamfanin Siemens, kamfanin da aka zarga da bayar da ma'kudan kud'ad'e cin hanci ga wasu manyan jami'an Nijeriya sun kawo ziyara, kuma 'Yar'aduwa ya tarbe su a Aso Rock Villa, yana mai annashuwa da sakin fuska. Wannan ya nuna cewa wula'kancin da aka yiwa Ihsanoglu da gangan aka yi; saboda shi ba d'an jari-hujjan Yammacin duniya ba ne.
Don haka na ke ganin wad'anda ke jan akalar Gwamnatin 'Yar'aduwa - wata'kila - ba da son ransu ya halarci taron OIC ba. Babu mamaki sune suka zugo CAN ta fad'i abin da ta fad'a duk da cewa surutai ne kawai marasa tushe bare makama.