Saturday, May 17, 2008

"Mun 'Daura 'Damarar Ya'ki Da Jahilci Da Zaman Banza"


Daga Muhammad K. Muhammad
Alhaji Lawan Alhassan Mai Warwaro shi ne shugaban ri'ko na 'kungiyar Ibrahim Katsina Foundation (wato 'Kungiyar Raya Unguwar Ibrahim Katsina) da ke 'Karamar Hukumar Jos ta Arewa. A wannan hirar da ya yi da Aminiya ya bayyana manufofin kafa 'kungiyar da kuma nasarorin da ta samu ya zuwa yanzu.
Aminiya: Menene ma'kasudin kafa wannan 'kungiya ta Ibrahim Katsina Foundation?
Alhaji Lawan: Dalilan da suka sa muka taru muka yi tunanin kafa wannan 'kungiya suna da dama 'kwarai. Kai da kan ka in ka lura [za ka ga] kullum duniyar ta mu 'kara ci gaba ta ke yi. Kuma ci gaba ba ya yiwuwa sai da al’umma; kuma ba ya yiwuwa da al’ummar sai an had'a kai. Duk sanda al’umma ta had'a kai, to za ta ci nasara a kan dukkan abin da ta sa a gaban ta. Amma daga lokacin da aka samu al’umma a d'aid'aikun su a warwatse, to karya su ba shi da wahala.
In ka lura, mu al’ummar mu ba mu saba da irin wad'annan 'kungiyoyi ba. 'Yan uwan mu da suke kudu ko yamma sun dad'e suna irin wad'annan tafiyoyin. Amma kuma daga lokacin da muka fara zuwa yanzu, mun yi 'karfin da 'kungiyoyin da suka shekara 50 ma ba su yi ba.
Aminiya: Ko za ka iya fad'a mana kad'an daga cikin manufofin wannan 'kungiya?
Alhaji Lawan: Manufar wannan 'kungiya ita ce: 'karfafa al’umma a kan al’amura, kamar ta wajen ilimi, ayyukan yi, dogaro da kai, wayar wa da mutane kai su san cewa su mutane ne—su san ’yancin kan su, zaman lafiya, da sauransu.
Aminiya: To wad'anne irin nasarori ku ka samu daga lokacin da aka kafa wannan 'kungiyar zuwa yanzu?
Alhaji Lawan: Alhamdulillahi, mun samu nasarori da dama. Na d'aya daga cikin abubuwan da muka fara yi, mun fara duba menene ya kan sa al’umma ta ci baya ko ta kasa ci gaba? Sai muka gane jahilci ne. Idan babu ilimi babu inda za a je. To sai muka ce mu fara d'aukar maganar ilimi mu sa a gaban mu. Sai muka duba al’ummar don mu ga ta ina ne za mu fara taimakawa ta 'bangaren ilimi? Sai muka ga akwai yara 'kanana wad'anda ba su zuwa makaranta, suna nan sai zaman banza, sai yawace-yawace. Sai muka kafa kwamiti mu ka ce ya binciko mana irin wad'annan yara, musamman marayu, da wad'anda iyayen su ba su da hali, amma suna da basirar karatu. Mu ka samu sunaye da dama daga ko wanne 'bangare na wannan maza'ba.
A wancan lokacin mun fara da yara kamar guda 40; muka sa su a firamare, muka biya masu kud'in makaranta, muka d'inka masu kayan makaranta, muka saya masu littattafai, kuma muka kafa kwamitin sa-ido (monitoring team) wanda ya ke zuwa makarantun nan ya tabbatar yaran nan suna zuwa kuma suna yin abin da ya kamata. 'Bangare na farko ke nan.
'Bangare na biyu shi ne sakandare. A wannan 'bangaren mun duba mun ga akwai yaran mu da yawa da suka gama firamare; su ma suna da bu'katar ci gaba amma babu hali. Muka taru muka yi doguwar shawara, muka ce akwai makarantu na ’yan uwa da abokan arzi'ki a gari wad'anda idan muka je muka ro'ki alfarma za a yi mana; saboda haka sai muka fara da makarantar uban mu, Alhaji Barau Abdullahi, mai suna Al-Hilal. Allah Ya taimake mu muka samu gurbin yara 10, wad'anda aka ba su daga 'karamin aji na d'aya (JSS1) har zuwa babban aji na uku (SSS3). Wato ba abin da za a biya a makarantar nan—su gudummawar su ga wannan 'kungiya ke nan.
Daga nan kuma sai muka tafi wata makaranta da ake kiran ta Trust International, ta Alhaji Tijjani Abdullahi. Nan ma—ko da yake ya ce shi ma akwai yaran marayu da ya ke taimaka wa da dama, amma tun da manufar mu ta alheri ce—ya ba mu [gurbin] mutum biyu.
Daga nan kuma sai muka tafi wajen wani d'an uwan mu Alhaji Hamisu Umaru, shi ma yana da makaranta mai suna Al-Haqq. Shi ma ya ba mu gurabe biyu. Sai kuma wani d'an uwan mu, Malam Idi Abubakar, yana da makaranta mai suna Al-Ikhlas. Shi ma ya yi mana alfarma, ya ba mu gurabe biyu. Dukka wad'annan su na nan a makarantun suna karatu.
Bayan waxannan kuma akwai wad'anda mu ke ta bi da dama, suka ga lokaci ya 'kure; amma bayan zangon karatu na ukun nan (third term), in Allah Ya yarda za mu samu gurabe da dama da za mu 'kara tura yara. Sannan a makarantun gwamnati ma muna nan muna 'ko'karin mu sa yara kamar guda 40. Mun tura ana ta yi mana 'ko'karin sama masu admission. Wannan 'kungiya ce za ta nemo kud'i ta biya masu kud'in makaranta, ta d'inka masu kayan makaranta, ta saya masu littattafai. Mu dai burin mu mu ga mun kawar da zaman banza, da jahilci da yaran mu ke yi.
Sannan muna da kusan mutm 50 masu bu'katar yin digiri. To suma mun bi jami’o’i kamar guda uku muna 'ko'karin cusa su. Sannan muna da wani uba, Malam Musa Muhammad, Limamin Abuja, shi ma ya d'ebi yara uku ya ba su tallafin karatu (scholarship) daga sakandare har zuwa jami’a—banda wad'anda na yi bayaninsu—Allah Ya saka mishi da alheri.
Akwai kuma yaran da suka gama karatu amma babu aikin yi. To su muna da ’yan uwa irin su Jalalu Arabi da Alhaji Umaru Sani, wad'anda su ke 'ko'karin taimakawa wajen sama masu aiki. Ta 'bangaren sana’o’i kuma muna da burin taimakawa; a hankali muna nan muna tunanin yadda duk jama’ar unguwa har ma da matan aure, za su amfana.
Sannan akwai wasu yara masu shaye-shaye, da ’yan sara-suka. Su kuma mun je mun samu Hukumar Ya'ki Da Mu’amala Da Miyagun 'Kwayoyi, NDLEA, da DPO na ’yan sanda don su ba mu gudmmawa don mu tabbatar mun kawar da wad'annan abubuwa daga wannan unguwa tamu. Yanzu haka ma shirin da mu ke yi za mu je mu gana da kwamishinan ’yan sanda don mu had'a kai mu tabbata al’umma ta zauna lafiya. Kuma muna 'ko'karin ganin idan rashin fahimta ya faru a unguwa tsakanin mutum da mutum, to kar a yi saurin zuwa wajen hukuma: a kawo wajen wannan 'kungiya in Allah Ya yarda za ta tabbatar ta sulhunta. Wad'annan kad'an ke nan daga cikin nasarorin da mu ka samu.
Aminiya: Babu shakka ana bu'katar kud'i don gudanar da dukkan wad'annan abubuwa da ka fad'a. Wad'anne hanyoyi wannan 'kungiya ta ke bi don samun kud'in da ta ke gudanar da ayyukan ta?
Alhaji Lawan: A yanzu dai 'kungiya ta na samun kud'in ta ne a tsakanin ’yan 'kungiya. Da farko, mun sanya cewa ko wanne mamba zai bayar da a'kalla naira 50 ko wanne wata. A cikin mu kuma, akwai wad'anda Allah Ya fifita su, wad'anda in wani abu ya taso za mu je wajen su, su cire abin da ke aljihun su a cikin arzi'kin da Allah Ya ba su su ce a je a yi.
Wannan abu da mu ke ta yi duka a jikin mu ne. Mu ya mu ne mu ke ta 'ko'karin samo wannan kud'i. Lokacin da muka fara wannan al’amari, mun fara ne da neman taimakon motar d'aukan gawa. To a wancan lokacin mun samu kud'i isassu, mun sayi wannan mota tana nan tana aiki. To kud'in da suka saura a wancan lokacin su ne su ka zama tsanin da muka taka mu ka fara yin wad'annan ayyuka.
Wad'annan ’yan hanyoyi su ne 'kungiyar nan ta ke bi a yanzu ta ke samun kud'i, amma nan gaba za ta fad'ad'a su in Allah Ya yarda.
Aminiya: Akwai wani taimako ne da ku ke samu daga gwamnati da kuma sauran jama’ar gari?
Alhaji Lawan: Ba mu fara tuntu'bar gwamnati ba tukuna; domin da muka fara 'kungiyar ba ta da kundin tsarin mulki (constitution), sai daga bayan nan muka samu. Yanzu muna 'ko'karin samun rajista ne a hukumar rajistar kamfanoni (CAC). Idan muka samo wannan rajista to mun samu sanda da za mu je gaban gwamnati mu nuna mata 'kungiyar ta kafu ta zauna da gindin ta. In Allah Ya yarda muna kan wannan.
Aminiya: A 'karshe wanne irin kira za ka yi ga al’ummar unguwa don su bayar da had'in kai ga wannan 'kungiya?
Alhaji Lawan: Ina kira ga al’ummar unguwa gaba d'aya su juyo hankalin su su ba wannan 'kungiya had'in kai. Wannan 'kungiya wacce idan suka dube ta da kyau za su ga cewa a duk garin nan ko Jihar nan, babu 'kungiyar da ta ke da manufa da niyya mai kyau kamar ta. Kuma 'kungiyar ta taso a d'an 'kan'kanin lokaci, ta ci nasarori da daman gaske. Saboda haka ina kira ga dukkan al’ummar wannan unguwa su ba wannan 'kungiya goyon baya; duk lokacin da ta kira su su amsa, duk lokacin da ta nemi gudummawar su ko wacce iri ce su bayar. Ba ma mutanen unguwa kawai ba; ina kira ga mutanen gari ne gaba d'aya. Yanzu misali mu na wa garin mu addu’a da ’ya’yayen mu, da kuma addu’ar zaman lafiya. Duk 'karshen wata mu kan taru a d'aya daga cikin masallatan unguwar mu, mu sauke Al-'Kur’ani, mu yi sadaka, mu yi addu’o’i Allah Ya zaunar da mu lafiya: Allah Ya zaunar da garin mu, da Jihar mu, da 'kasar mu lafiya. Kuma ’ya’yayen mu Allah Ya shiryar da su Ya ba su ilimi mai albarka.
Jaridar Aminiya, 11 ga Jumada Ula, 1429 (16 ga Mayu, 2008)